Samun ƙungiyyar Matan Masana'antar Kannywood Abu Mai Matukar Amfani - Inji Saratu Gidado | test 2 -->


PROMOTE MUSIC/VIDEO      ADVERTISE ON EL


Shortenlink and get Paid




    Thursday, March 29, 2018

    START HERE
  • Samun ƙungiyyar Matan Masana'antar Kannywood Abu Mai Matukar Amfani - Inji Saratu Gidado
  • STOP HERE
    Shortenlink and get Paid
    Sartu Gidado Daso ta bayyana qungiyoyin da mata yan film
    ke samarwa a yanzu domin taimaka wa ’yan fim da sauran
    jama'a a matsayin wani mataki na ci-gaba da harkar ta
    samu.

    Wannan bayani ya fito ne daga bakin fitacciyar jaruma Hajiya
    Saratu Gidado a lokacin da ta ke tattaunawa da wakilin
    mujallar Fim dangane da irin yanayin da aka samu a cikin
    masana’antar na bullowar wasu kungiyoyin mata da ke
    taimaka wa jama’a marasa karfi.

    Saratu (Daso), wadda a yanzu ita ce Jakadiyar Sarkin Kano,
    ta ce, 

    Wadannan kungiyoyi na taimaka wa marayu da
    marasa karfi, musamman yara kanana da wasu da aka mutu
    aka bar su. Wasu na yawon bara, wasu na yawon talla.

    “To gaskiya kafa kungiyar ya burge ni. Na ji dadin yadda su
    ka zauna su ka yi tunani su ka samar da wadannan
    kungiyoyin.

    Ka san babu mai iya wa mutum sai Allah. To amma dai ko
    yaya ka samu ka taimaka wa na kasa da kai ka na da lada
    mai yawa. Kuma kai ma da ka ke da hali ba ka san yadda
    za ka kasance a gaba ba, amma dai alheri ba ya faduwa
    kasa banza.”

    Ta ci gaba da cewa, “Yanzu wannan aikin alheri da aka fara
    mutane za su san cewa ’yan fim su na da tausayi, mu na
    taimakon bayin Allah mu ma. Duk da ake yi mana kallon
    wasu mutane na daban, mu ma mu na aimakon, don haka
    yanzu mun fito mu na taimaka wa mutane kamar yadda ake
    gani su na yi duk da dai ba na cikin kowace kungiya saboda
    hidima ta ni ta yi min yawa don haka ni nawa taimakon ba
    a bayyane na ke yin sa ba. Don haka ban shiga cikin
    kungiyoyin ba, amma ina da labarin abubuwan da su ke yi,
    kuma ina goyon bayan su dari bisa dari.”

    A game da kasa kungiyoyin kashi-kashi, kowa ya na yin
    tasa, Saratu ta ce, “To ai ba an rabu ba ne kuma ba ana
    fada ba ne, kowa ya na da tsarin sa na yadda zai bayar da
    nasa taimakon.
    “Haka idan wata kungiya ta kai tallafi ga iyalan ’yan fim
    da aka rasu aka bar su da kuma wadanda ba su da karfi,
    wata kungiya kuma ta kai tallafi gidan marayu, wata kuma
    ta kai tallafi asibiti, ka ga ai an samu ci-gaba. Kowa da irin
    tallafin da ya ke ganin zai iya bayarwa ga jama’a. Don
    haka samun karin kungiyoyi masu bada tallafi abu ne mai
    kyau, kuma ci-gaba ne.”
    Daga karshe Saratu ta yi kira ga al’umma da su bada
    gudunmawar su, musamman ma ’yan fim, domin ganin
    wadannan kungiyoyi sun samu nasarar da su ke bukata ta
    taimaka wa mabukata.
    Disqus Comments
 


Looking for something? Search below

CHECKOUT THESE HOT SECTIONS ON 9MW

...... ...

...... ...


Pages